Tuesday, September 20, 2016

HANIFA 2


  Bilal ya shigo gidan su hanifa,yaga hanif yana dukan hanifa,yayi sauri ya reke shi,hanifa Na kuka,jikin ta duk jini,bilal Yakama hanif yafita dashi daga cikin gidan,yace haba hanif kafara shaye shaye ne?wannan wani irin rashin imani ne? Ya zaka Kama yarinyar mutane kana duka kamar kasamu dabba,da wanne zata ji,rashin iyayen ta,KO wanne?gaskiya kabani kunya,baka kyauta ba,hanif kamar bada shi ake ba,ya ture bilal ya bude motor shi yashiga ya fita abun shi,bilal yashiga ya same hanifa yabata hakuri,yace sutafi asibiti,hanifa tace a'a baza ta Iya zuwa asibiti ba,anan dai bilal ya Kira matar shi akan tazo gidan su hanifa,bayan ta iso,bilal yace taje ta kula da hanifa,hakan akayi kuwa.Hanif yayi sati uku baya gida,ranar da yadawo,yashigo yana kuka,hanifa hankalin ta yatashi sosai,saboda bata taba ganin shi a cikin irin wannan yanayi ba,hanif yaba hanifa hakuri,yayi nadama akan ya zalunci ta,kunyar ta yake ji baisan KO zata Iya yafe masa ba,cikin ikon Allah ta gafarta masa,bayan sati daya bilal yazo gidan su,abin mamaki,yaga yanda su hanifa ke zama lafiya kamar basu bane suke fada kwanaki,yayi hamdala yace hankalin sa zai kwanta yanzu,abin Sha'awa in kuka gansu.
  Bayan wata biyu,hanif yace zai sake aure,hanifa tace sam,bai isa ba,yace shida gidan sa,inba zata Iya zama ba,ta debe kayan ta,takama hanya,Hanifa haka tayi hakuri,akayi aure,anan fa aka bude shafin sabon wulakanci,amaryar hanifa Hauwa,ba mutunci ne da ita ba,kuma bawani Abu bane yajawo hakan,hanif ne yasata haka,Dan gaskiya har ga Allah tana son hanifa,anma da taji ance za'ana fita da ita kasar waje malama Hauwa Kam tafara shuka rashin mutunci,hanif baya kwana dakin hanifa,baya cin abincin ta,baya Mata magana,in ta mishi magana ma,harara ke raba su,akwai ranar daya daga hanu zai mare ta,Hauwa tace malam kul,kasake ka mare ta,in zaka Mata rashin mutunci kayi Mata,anma banda Mari,Dan KO makiya Na,banason Inga an mare shi,balle ita wannan,hanif ya girgiza kai,yafita,hanifa tace wa Hauwa ta gode,ya salam,hanifa abin tausayi,kamar baiwa,ta rame,tayi wani iri,ba kyaun gani,kawai tana rayuwa ne,anma bata Iya sa kaya Mai kyau,Ina bilal yake?Allah sarki bilal,shikam aiki yakai shi cross river,tunanin shi Hanifa Na cikin dadi,kullum in ya kira tace mishi lafiya,in ya Kira hanif ma haka,bayan hanifa tayi godiya wa Hauwa,sai Hauwa tace Mata bance ki gode min ba,kije ki kwashe wanke wanke kiyi,ki kuma Gera min daki,Abu kamar asiri,haka Hanifa takama hanya tafara aikin da aka sata,akwai masu aiki anma ba aikin da sukeyi Hanifa ke komai,Hauwa tashiga daki tana kwance,sai hanifa tazo Gera Mata daki,suna hada ido da hanifa tausayi ya kamata,tace Hanifa bar Gera,kinci abinci ? Tace a'a banci ba,tace muje kici abinci toh,Hauwa ta zuba wa hanifa abinci,tace yau Kam Ina son kiyi kwalliya ingani kinfi ni kyau KO nafiki irin da wasan nan,hakan akayi,abin dariya abin tausayi, kamar wata yaya da kanwa,hanifa tayi wanka ta chanja kaya bata wani kwalliya ba,anma Hauwa tace,haka kike da kyau yaya hanifa,gaskiya banjin dadin yanda nake ganin ki ahaka,sai ga hanif yashigo yagan su,ya kalle su,azuciyar sa yace da sake kenan,watau sun hada Kai dan su cuce ni,Hauwa taje ta same hanif,tace abinda suke wa hanifa ba kyau,tagama mishi wa'azi yace kin gama tace eh,yace toh Dan ubanki kafin tace wani Abu ya hau ta da duka,ya Mata duka takasa tashi,hanifa najin haka ta gudu ta buya,ya nema ta yarasa,yaje Boys quarter (BQ) Chan dama yace takoma DA zama,bai ganta ba,a Daren dai Hauwa tasha duka,washigari ya sake Aure,sunan ta fatima.
  Bayan wata biyu da auren fatima,rikici kullum tsakanin fatima da Hauwa,haka ake cin kaniyar Hauwa da hanifa acikin gidan,Hauwa ba hakuri,Fatima kuma ba imani,watau wani Rana da akayi ma Hauwa duka,aka karya hannun ta da kafar ta,bakin ta ya kumbura ba halin magana,kamannin ta ya chanja,ba abinda hauwa ke tunawa sai rashin mutunci datayi wa hanifa,tace tabbas ta zalunci kanta,tunda Hanifa KO karya ta bataba yiba,ahankali dai hanifa tana jinyar Hauwa har tafara samin sauki,Hanif KO ajikin shi,Allah yajarabe shi da son Fatima kamar zai mutu shi kuma,intace yayi Abu haka yake karkarwa saboda baison bacin ranta,Fatima tasa ya sayar da company furniture's hanifa,haka akayi,kawai ya dinga sayar DA asset in hanifa,yace nashi ne ai,bana ta bane,wani tashin hankalin kenan fa.
    Watarana hauwa suna hira da Hanifa,Hauwa tace yaya hanifa kibani labarin rayuwar ki,hanifa tace baki da lafiya,zakiso jin labari Na kuwa,tace mai zai Hana,haka suka wuni tana bata labari,tagaji tace zata cigaba washigari,Hauwa tayi kukasosai,ta tausayawa hanifa,ta nema gafaran hanifa,takuma yafe Mata,Fatima tashigo cikin dakin tace hanifa watau samun wuri KO,kinyi wanke wanke ne kika zo kika zauna anan ,Hauwa ba halin magana,an koya Mata darasi,tana fama da jikin ta,Fatima tace muje ki Gera min daki,haka akayi kuwa,yau ne gobe shiru,ranar dai hanifa bata kwana a boys quarters ba,Hauwa bata Iya tafiya,tana ta salati kar Abu ya faru da hanifa,hankalin Hauwa ya tashi sosai,haka takasa Bacci,sai washigari da safe, hanifa ta shigo BQ,Hauwa tace lafiya,hanifa tace matan nan aiki tasani,takuma hani ni inzo BQ,haka Na kwana Ina aiki,ba abinda banyi ba,na wanke toilet,kayan ta,nayi abinci,aiki dai kawai,Hauwa tace kinganni banyi Bacci ba,hanifa tace meya Hana ki Bacci,tace Ina tsoron kar abinda ya faru Dani ya faru dake,wa zaiyyi jinyar wani kenan,suka fashe da dariya,Hauwa tace shi Mai Gidan Fatima fa,hanifa tace auw!! Yanzu mai gidan Fatima ne,ba Mai gidan Mu ba,sukayi dariya,tace yatafi england, yau Zai dawo,haka dai suka ta zolayar juna suna dariya.
  Bayan wata biyu,Hauwa ta warke,suna ta famar aiki,Fatima ta sa hanif ya chanja sunayen company,estates, motor,komai da kuka Sani zuwa sunan ta,hanif kuma Na masifar son ta,bayanda ya Iya,kudin account inshi komai tace sai dai yayi transfer insu zuwa account inta,haka akayi,takai ta kawo katin waya sai ya tambaye Fatima tukun zata bashi kudin,tasa shi wankin motor,shara,girki,abin sai yafara ba su hanifa mamaki,in yana aiki,sai suce mishi sannu da aiki mijin hajiya,takai ga su hanifa basu wani aiki sosai,komai hanif keyi,hanif yazamo driver,Dan aika,bayada bakin magana,dukiya sun zama Na Fatima,komai DA komai,Dan haka cin arziki yake,akwai watrana da tasa shi aiki,Bacci ya dauke shi baiyyi ba,haba ta same shi,ta wanka mishi Mari,hanif ya daga hanu zai Rama,tace in ka kuskura katabani,sai nasa an kulle ka,Inga waye gatan ka,Dan ubanka,su hanifa da Hauwa Na gefe,sai murna,gaba ki daya in kuka ga hanif yafita hankalin sa,takai ta kawo hanif daki daya suke kwana da Mai gadi,abin dariya,Mai gadi kuma hajiya tace kar ya tausaya masa,akarshe dai,kusan kowa ya Rena shi,Mai gida ya zamo bawan gida.
   Bayan sati daya,Fatima ta Kira hanif, tace hanif nasan ban kyauta maka ba,kayi hakuri,nayi haka saboda in gwada ka KO kana sona ne,KO kana da hakuri,Kuma wallahi kaci jarabawa ta,dan haka kaga wannan documents in dukiyar,Zan dawo maka dasu,anma da sharadi daya,Zan sake gwada ka in kaci jarabawar ka ta karshe shikenan,yace koma menene,ya aminci,tace yaje yasa kayan shi daya fiso,hakan akayi,hanif yayi wanka,yasa sabon kaya kamar ango,Fatima ta kira hanifa da Hauwa,tace kuje dakin ku,kuma kuyi wanka Ku chanja kaya da kuka fi so,abin kamar drama Hausa film,akayi haka,sun gama kwalliya sai akayi sallama,wa muke gani haka kamar bilal da Amina,haba hanifa ta rungume Amina,ta fashe da kuka, bayan sun gaisa,Amina tace kukan meye haka hanifa,tace kukan murna ne,suka Mata dariya,hanif suka gaisa da bilal,yace malam bilal ka bata shiru, yau shekara uku kenan KO hudu,yace meet my wife,Fatima and Hauwa,bilal Kai malam ka aure bamu Sani ba,yace kasan aure zuwa take,suka dariya,suka zauna suka ci abinci bayan sun gama cin abinci,Ana ta hira,Fatima ta tashi tafita,ta koma parlor, tace in sun gama tana son magana da kowa,hanif yace haba Fatima kijira mana baki ga akwai guest bane, Fatima tace malam ba ruwana da guest, hanif yaga tabbass Fatima ba Allah a zuciyar ta,haka suka taso suka same ta a parlor, tace barkan Ku bakin Mu,batare da bata lokaci ba,hanifa da Hauwa kuzo nan Ku tsaya,bilal da Amina,suna kallon ikon Allah,namanta ban fada muku ba,bilal yazo da yaron shi Mai suna tahir,shekaran shi biyu,ya Kuma sa Mishi sunan saboda sunan mahaifin hanifa ne.hanifa da Hauwa suka tsaya inda aka umurce su,tace ya Kai mijina hanif,kace zaka Iya komai akaina,hanif yace tabbas,tace kalle matan nan,Ina son ka fada min tsakanin ka da Allah wace tafi kyau,yace ban gane Mai kike nufi ba,tace eh ka fada min wace tafi kyau,yayi shiru,ya kalle su,yace hanifa tafi kyau,yace Dani da hanifa fa?haba ai ba hadi kin fita kyau,yana dariya,yace ko ba haka ba abokina yana magana da bilal,ya salam inji bilal,ikon Allah,ya goge idon shi,abin kamar mafarki,yaga fa dagaske ne,ba mafarki bane KO film,ya girgiza Kai,Fatima tace hanif nayi Kama da wasa nake maka,yace kiyi hakuri,tace kabani amsa ta,nida hanifa wayafi kyau,hanif yace ba hadi,hanifa tafi ki kyau,Fatima tayi murmushi,tace Ina son ka sake ta Saki uku yanzu nan,kowa yayi salati,tace ka hada da Hauwa,kowa saki uku-uku,bilal yace ke Fatima baki isa ba,bawanda ya isa yasa a sake hanifa,in kuma aka sake ta kowa zai bar Mata gidan ta,har Kai hanif,Fatima tace wani gida?gida ai nawa ne,bilal gida naki?taya gida ya zamo naki? Tace hanif kabashi labari,hanif yace hanifa kibashi labari,hanifa tace katuna lokacin da muke fada,daga baya hanif yazo ya shiryu,muka daina fada? bilal yace eh,meyefaru Ina jin ki,hanifa tace alokacin yasa Na chanja sunan companies, ima,Estate,all my asset to his name,which I did,ashe tuban muzuru ne,hanifa sai kuka,bilal yayi salati,yace hanifa why? Why? Ya salam,anma hanif Allah sai ya tsene maka albarka,sai ka shiga wuta wallahi, bilal bai san Mai zaice ba,hanifa tace shi kuma hanif ya chanja sunan shi yaba Fatima,ya salam,Fatima tace toh malam kaji yanda gida ya zamo nawa?tace hanif kasake su KO kabar min gida,hanif yace hanifa Na sake ki Saki uku,Hauwa Na sake ki Saki uku,suka fashe da kuka,Fatima tace saura ni,hanif yace ke kuma,tace eh,ai kasan bazan Iya zama da mijin hajiya ba,ka nuna min zaka Iya yin komai akan dukiya,wallahi da kaki sake su da kaci jarabawa na,anma ka fadi Dan haka ga cheque in 300million in kasake ni,kaga baka fadi ba,hanif ba tunani biyu ya sake Fatima,yana sake ta Saki uku,Amina ta fashe da dariya,abin yaba bilal mamaki,haba Fatima ta rungume Amina,kallo ya koma sama.
    Bilal yace dama kun San Juna ne?Amina tace wannan sister Ina ce Fatima baka Santa ba,nasan zakuyi mamaki,maganar gaskiya shine,mahaifin hanifa ya taimaka muna a rayuwa,wani lokaci an Kore Mu a gidan haya,shi ya dauke Mu yaba Mu gidan dakasan Mu dashi,shi ya biya wa Fatima kudin makaranta complete har tagama,saboda baisan yanayin rayuwa ba,lokacin Dana fahimce halin da hanifa ke ciki,shine mukayi magana da Fatima,wallahi banma San Fatima ta kwarai haka ba,bilal yace mafarki nake ne?Fatima tacigaba da basu labari,komai da komai,tace hanifa Gare ki,hanifa tace Hauwa kin tuna Ranar Dana ce miki aiki nayi Fatima ta hana ni dawo daki,hauwa tace eh,toh ranar Fatima tabani labarin komai,idan kin Lura Ina ta murmushi kina tambaya menene?ince babu,Hauwa tace Na tuna,tace Allah Mai iko,Fatima tace Hauwa ki yafe min,wallahi karfin hali nayi,Ina jin zafin abinda Na muku haka Na danne zuciya ta,suka rungume juna ,bilal yace Amina Allah miki Albarka,Allah yasa ki aljanna,Allah miki Albarka,bilal yace hanifa ga daddy ki Na kawo miki,tace Kai,baba nane ban Sani ba,ta dauke tahir,Fatima tace ga documents, ya bilal tunda lawyer ne Kai,sai a chanja suna su koma Na hanifa.Hanifa tace hanif Mai Kati,akwai card ne,kabani MTN da GLO Na 1500 each,haba suka fashe da dariya.aka kore hanif agidan KO takalma bai fita dashi ba,yakoma matsiyacin sa,yafi da tsiyatancewa,bayan wata biyu,hanifa da Hauwa,da Fatima sunci kwalliyar su,in kuka gansu kamar hasana,husaina,da gambo,hanifa ta basu kudi,gida,motor,tasa suna managing wasu company ta,kowa Na zama lafiya,hanif kuwa bara ya koma yi,abinci ma wahala samu take mishi,yazo tsallake titi motor ta bige shi,ankai shi asibiti,akace sai an yanke kafar sa guda daya,sanadiyan hakan ma yarasa idanun sa guda daya,haka Allah yayi dashi,yana nan yana bara.

Karshen Labarin hanif da hanifa kenan,nida Na rubuta cmc,nagode  ,KU KASANCE TARE DANI A KO WANI LOKACI NAGODE SOAI KU KARANTA SAURAN LABARAI,KAR KUMANTA KUYI COMMENT NAGODE

HANIFA 1


 Hanif Na zaune a inda yake  sayar da recharge cards,yaga wata budurwa ta jefar da wallet inta,batare da tasani ba,tashiga motor,tayi tafiyar ta,hanif yayi sauri ya dauko wallet inta,ya tare taxi,yabi baiwar Allah nan,yana isa traffic yaga an tsayar dasu ba halin tafiya,ya daga Kai sai ya hango motor wannan yarinyar,yace wa Mai taxi yana zuwa,anan ya sauka yaje ya kwankwasa glass in motor yarinyar,ta kalle shi,tana sanye da bakin(black) madubi,ta saukar da glass in motor,tace kayi hakuri,bani da kudi,ita a tunanin ta Mai bara ne,yace kiyi hakuri ba bara nazo ba,kin jefar da wallet inki ne tun a plaza,shine Na kawo miki,ya Ciro wallet inta ya mika Mata,tace ya salam nagode sosai,anan traffic ya sake su,mutane suka Fara horn,yace mata sai anjima yatafi yabar ta,ita kuma ta shiga motor tayi tafiyar ta.bayan kwana biyu da faruwar haka,wannan budurwa tasake zuwa plaza, bayan tagama abinda tazo yi,har tafito waje sai ta hango hanif yana sayar da recharge card bakin hanya,ta tsaya tace Mai Kati kawo min MTN 1500,Glo 1500,hanif yazo aguje yana isowa yaga wannan budurwar ce,yace hajiya Ina wuni tace lafiya,dama anan kake aiki,yace eh,tace nagode fa da ranan,inda Ana samun mutane irin Ku da duniya ta zauna lafiya,hanif yayi murmushi,yace nagode hajiya,ta mika mishi wayan (phone) inta,tace yasa Mata card in,bayan yagama tace yasa number wayan shi zata Kira shi zuwa anjima suyi magana yanzu sauri takeyi,hakan akayi kuwa,bayan yagama,tace ya sunan malamin,yace hanif suna Na,tace ikon Allah,suna Na hanifa,Zankira ka anjima,anan suka rabu.
   Aiki yayi wa hanifa yawa,ta manta da zance kiran hanif a waya,dayake hanifa ke kula DA company Baban ta Na furniture's,mahaifin Hanifa Mai kudi ne sosai,ita kadai Allah ya basu,bata da brother KO sister, hakan yasa ake matukar ji da ita sosai,mahaifin hanifa nada gidajen mai,company, estate a Nigeria da kasashen waje,england,Dubai,America,da wasu kasashen.hanifa yar gata ne sosai yanda Baku tunani,batasan wani aikin wahala ba,komai yi Mata ake,anma hakan baisa bata tausayin talaka ba,tana da kyauta da kuma kyautatawa,tana zaune a office sai ta tuna akan tayi alkwari zata Kira hanif,anan take ta dauko wayar ta,takira shi,suka gaisa tace Mai zaiyyi ranar asabar,yace ba abinda zaiyyi,tace tana so sufita,Dan haka Ina zata same shi,yabata address, suka gama wayar su,ranar hanifa ta dawo gida late,bayan ta huta,mahaifiyar ta tace,yau kin jima a aiki,suka ta hira dai Baban hanifa shima ya shigo,ya same su akacigaba da hirar dashi,tace mama ai ban baki labari ba,nan ta kwshe labari haduwar su da hanif tagaya musu,tace kuma tayi dashi zasu hadu ranar asabar,tana son suje park,Baban hanifa yace Mai zai Hana ki kawo shi gida kawai,tace haba baba bamu wani San Juna bafa,with time dai,haka suka ta hira,Bacci ya dauke hanifa,maman hanifa ta daga ta Zuwa daki,dayake karamin jiki ne da ita,ba nauyi.

      Ranar asabar,Hanifa ta hadu da hanif,sukayi hira sosai,yabata labarin rayuwar sa,labarin muguwar kishiyar maman shi,wahalar daya sha,da kyar yayi polythnic,abin tausayi dai labarin nashi,yanda har ya shigo abuja yafara sana'ar sayar da card,wahalar dayasha a rayuwar sa,hanifa ta matukar tausaya masa,haka dai suka ta hira daga karshe taje ta ajeye shi agida a motor ta,bayan ta dawo gida,ta huta,kamar yanda ta Saba,suka hau hira da iyayen ta,tabasu labarin Hanif suka tausaya mishi,Baban hanifa yace kice mishi Ina son ganin shi,hanifa tace inshaa Allah zan fada mishi,a daren kafin hanifa tayi bacci ta Isar da sakon mahaifin ta zuwa ga hanif.
     Mahaifin hanifa yana office sai ga hanifa tashigo,tace baba ya aiki?,yace lafiya my daughter,ya kike?hanifa tace lafiya,tace hanif shigo mana ya ka tsaya bakin kofa,Baban ta yace keda mutumin ne ,shigo mana malam hanif,zoka zauna,bayan hanif ya zauna,yace sectary ta kawo mishi drink,hanif yana ta kallon cikin office,abinka da bakauye,yakasa shan drink inma,yana ta kalle kalle,mahaifin hanifa yace malam hanif,naji labarinka Kuma Na tausaya maka,I heard kayi polythinic KO? Mai ka karanta?hanifa yace business administration, baban hanifa yace,very good,kazo da CV ka gobe,kafara aiki gobe a company nan,hanif yayi hamdala yata godiya ,yace Allah saka da alkhairi alhaji,hanif ya fashe da kuka,hanifa ta kalle shi,Kai kuka kake,tayi mishi dariya kabani kunya,baban hanifa yace kukan murna ne,stop crying malam hanif,yanzu Zan fita,zaku tafi KO kuna nan har ingama meeting Ina?hanifa tace,abinda ya kawo Mu kenan tunda kun hadu no need,nima Ina da aiki a office, sukai sallama,suka tafi.
   Hanif yafara aiki company Baban hanifa,yana kokarin gaske,ga rikon amana,ga ibada,hakan yasa baban hanifa yakara sonshi,watrana Baban hanifa yayi ciwo sosai,hanif ke zama dashi a asibiti,yana kula dashi har Na tsawon wata daya,Baban hanifa yaji ya Kara son hanif sosai,bayan alhaji tahir mahaifin hanifa yaji sauki,ya dawo aiki,yayi promoting hanif as manager a company,aka bashi gida,motor,hanif yayi murna sosai,yanda alhaji tahir ke kula dashi kamar Dan cikin sa.
     Hanif yashigo gidan su hanifa yaganta suna hira da wani saurayi,yanda ya kalle hanifa,azuciyar ta,tace lafiya dai ko wannan kallo haka,bayan ta fahimce kishi hanif yake,tace hanif meet my boyfriend bilal,hanif ya kalle su KO amsa su bayyi ba ya shiga cikin gida,haba Hanifa sai dariya,bilal yace malama zaki hada ni fada da bawan Allah,ita kuwa sai dariya,hanif yafito zai tafi tace Kai malam zo nan,wani irin wulakanci ne wannan,Zan hada ka da mutum Ku gaisa bazaka mishi hello ba,wannan ai kauyanci ne,KO nice Na bata maka rai,Ina maka magana kana sha min kamshi,hanif baice Mata komai ba,sai ta dauko wedding card ta mika wa hanif,gashi wedding card Inane da bilal,hanif ya karba zai tafi,hanifa tace ka bude ka gani,hanif ya bude yaga,sunan bilal da amina,sai yayi murmushi,yama rasa Mai zaice,hanif yace malam bilal aure zakayi kenan?bilal yace inshaa Allah,abinda ya kawo ni kenan Na kawo mata wedding card,hanif yace Allah yasanya alkhairi,and I'm so sorry for my attitude, kuyi hakuri,bilal yayi dariya yace kar kadamu abokina,zantafi now,sai naganku ranar aure Na,sukai Sallama.hanif yayi wa hanifa magana ta juya mishi baya taki kula shi,alamar tayi fushi da kyar ya shawo kanta,tace Dan meyasa zai Mata haka,hanif dai yabata hakuri,tace shin ni budurwar kace ma da kake kishi akaina,duk sanda kaga wani yana min magana kata hada rai,in sona kake kafada mana,KO kafito ka aure ni,ita duk wasa take,hanif yace haka kika ce,tace eh,yace tafaru ta kare,yakama hanya yashiga cikin gidan,hanifa tace Kai wannan ba hankali Gare shiba,tabishi cikin gida,koda ta isa sai taji hanif Na magana da Baban ta akan yana son ya aure hanifa,alhaji tahir yayi murna sosai,hanifa ta shigo suna hada ido da hanif kunya ya kamata,ta gudu daki,alhaji tahir yayi dariya yace ikon Allah,anan dai akace ya turo iyayen shi,ayi magana,hakan akayi kuwa har aka daura aure.
    Bayan an daura aure Hanif da hanifa in kagansu abin Sha'awa,hanif baya Iya tafiya KO Ina batare da hanifa ba,acikin watanni shida in kuka ga irin soyayyar da sukeyi abin baya misultuwa,alhaji tahir yace wa mahaifiyar hanifa gaskiy Mu gode wa Allah,kalla yanda hanif ke kula da hanifa,yaron nan Dan Albarka ne,haka suka ta yabonshi,tafiya yakama Alhaji tahir,yace zai tafi da mahaifiyar hanifa,alhamdulilah sun tafi lafiya,hanifa kuwa da  hanif suna famar shan soyayyar su kamar tattabaru,ranar da alhaji tahir zasu dawo suka Kira hanifa sukace suna hanya,bayan sun iso airport, suka Kira Hanifa sukace gasu a Nigeria, zasu karaso gida,bayan hour daya sai ga kira ya shigo,hanifa ta dauki wayar ta amsa,tayi salati,hanif yace meyefaru hanifa,tace baba,baba,su baba sunyi accident,suna asibiti,hanif yayi salati,yace mutafi asibitin,isowar su keda wuya hanifa taga Ana rufe fuskar mahaifiyar ta,ga alhaji tahir numfashi sama sama,yace hanifa,hanif,Ku reke amanar junar ku,hanif ga hanifa amana,idanuwar hanifa cike yake da hawaye,takasa ce komai,alhaji tahir yace hanif,ka reke amanar hanifa,so uku ya mai'maita,ke kuma hanifa,duk abinda mijin ki yace kiyi kar ki bijire mishi,suka ji yayi shiru yana kallon su yana murmushi,sunkai minti biyu ahaka,likita yasa hanu ya rufe mishi fuska,hanifa takasa cewa komai,tana tsaye,sai tayi dariya,tace yau first of April shine zaku mini April fool KO,doctor har dakai za hada baki,nagode,tasake dariya,tace Ina phone Ina yake,Bari in Kira mama Na,nasan tana england,tasake bude mayafin DA aka rufe mahaifiyar ta,tace wannan Na Kama da mama Na,anma ba ita bace,wannan dai baba nane,anma bacci yake,hanifa ta rekeci ta fita cikin hankalin ta,anan tayanke jiki ta fadi aka dauketa aka kaita gadon asibiti,sati biyu tayi tana coma,abin tausayi,cikin ikon Allah ta farfado,haka dai masu gaisheta suka cigaba da zuwa.
  
      Bayan shekara daya da rasuwar iyayen hanifa,in kunganta zakuce ba ita bace,takasa sakewa,yawan mafarki,ta rame,ga tunani,hanif yadaina zama da ita sosai,sai karfe goma dare yake Dawo wa,inta mishi magana yace so kike in zauna agida kamar jariri,anan fa aka Dan Fara samun matsala tsakanin su,tun yana dawo gida karfe goman dare,yafara Dawo wa karfe dayan dare,abin sai cigaba yake,watrana sai asuba yake Dawo wa,watrana kuwa sai washigari,abin yafara damin hanifa,tace da wanne zata ji,mutuwar iyayen ta KO wulakanci da hanif yake Mata,tun tana mishi magana yana jinta,har takai ga in ta Mishi magana zai ture ta,akazo lokacin da hanif yana daga hanu ya mare hanifa,sai yayi kwana biyu baya gida,in yadawo yata warin giya,kayan jikin sa kamshin turaren Mata,ranar bilal yazo gaishe su,yana ganin hanifa yasan akwai matsala,yace kodai rasuwar iyayen ta ne,yamata fada tadaina tunani,dayake yazo tare da matar shi,banyan matar shi sun shiga dakin Hanifa sai ta Lura da jikin Hanifa akwai rauni ,fuskar ta akwai alamar an mare ta,anma da ta tambaye ta,tace Mata babu komai,bayan su bilal sun koma gida,matar shi tace bilal,Mai ka Lura da hanifa,yace inaganin tunani ne kawai yamata yawa,kinsan ita kadai iyayen suka Haifa,matar bilal ta kwashe labari ta fada mishi komai,bilal yace in har hanif yayi haka yacika azzalumi,zanje in same hanifa in tambayeta kozata fada min,matar shi tace Allah yasa.Bilal Yakama hanaya zuwa gidan su hanifa,yana shigowa ya tarar da hanif Na dukan hanifa.

Anan Na kawo karshen kashi Na daya ni Mai rubutu Cmc,nagode sosai Masu karanta labari Na,KU KASANCE TARE DA BLOG INA DOMIN KARANTA LABARAI MASU DADI,KAR KUMANTA KUYI COMMENT 

Sunday, September 18, 2016

AMIRAH

Amirah!! Amirah!! Amirah!! Amirah!kitashi Baccin ya isa haka,kitashi kiyi sallah,amirah tace haba mama,dan Allah meyasa bazaki daina tashina da safe bane,sai mutum Na Bacci zaki wani dame shi,maman amirah tace kiyi hakuri naga Rana yafito ne kuma kina kwance har yanzu,yakamata ko bazaki wanke wanke da shara ba,kitashi kiyi sallah,amirah tayi tsaki,ta tashi tafita daga dakin,maman amirah tace Allah ya shirya min ke amirah, bansan Ina kika samo wannan halin naki ba.
 
Karfe biyar na yanma,amira ta shirya zata fita,mahaifiyar ta,tace amirah Ina zakije,bakiga yanma yayi bane,yakamata ki tsaya kitayani aiki,kinga dai kannen ki yara ne ba abinda zasu Iya yi,amirah kamar bada ita akeyiba,tasa headphone a kunne tayi tafiyar ta,maman amirah ta girgiza Kai,tace Allah shirya min ke amirah ta,tace Allah yajikan mahaifin ki,nasan da yana Raye,hakan duk bazai faru ba,anma ni dayake kin raina ni,shiyasa,haka take ta maganar ta.karfe biyun dare maman amirah Na zaune tana jiran taga dawo wan amirah,nan bada jimawa ba,ga motor a kofar gidan su amirah,an sauke ta,sautin kida natashi daga motor,amirah tashigo gida,taga maman ta Na zaune Na jiran ta,gudun magana,yasa mamar bata tambaye ta daga ina tafito ba,haka dai mahaifiyar amirah tacigaba da hakuri da ita,wulakanci yau daban na gobe daban,abin mamaki shine,ya mutum zai maida mahaifiyar sa kamar bawan shi,mutanen unguwa suna kirar amirah suna Mata wa'azi akan tadaina abinda takeyi,tun tana ce musu tagode da wa'azi,akazo lokacin da inka Mata magana ma zagi zai raba Ku,akwai lokacin da limamin unguwan su yakira ta,yagama Mata wa'azi haba sai amirah tasa ihu,mutane suka taru,akace Mai faru,tace liman ne yace yana son ya sadu da ita,wai tana Da jiki siffar irin matan dayake so,karya dai, ba irin abinda bata fada ba,wasu suka yarda wasu kuma sukace karya ne,haka dai da kyar akabata hakuri ta tafi.
   Ciwo yakama mahaifiyar amirah,bamai kula da ita,ba kudin sayan magani,yaranta biyu kanana ne,daya mai shekara uku sai daya shekara biyu,haka dai ta kokarta tafita da kyar takai kanta chemist, aka bata magani batare da an karba kudin ta ba,tana ciki wannan halin amirah tazo gida ta kwashe kayan ta, zata bar gidan,maman amirah tace amirah Ina zaki je,bakiga banda lafiya bane? Ai KO tafiya zakiya kijira in warke,dan Allah kar kibarni cikin wannan hali,amirah tace mama ciwo jikin ki yake banawa ba,Dan haka ke ta shafa,in ma mutuwa zaki Allah jikan ki,nidai kinga tafiyata,har takama hanya zata fita sai ta dawo ta ajaye dubu goma tace ga wannan kiyi amfani dashi saboda ba lalle musake haduwa nan kusa ba,tace Bari ma muyi photo,abindai da iskanci,haka tayi musu photo itada kannen ta da maman,takama hanya ta fita,maman amirah tace Allah ya shirya min ke.

     Amirah tabi saurayin ta suka tafi Lagos,bayan wata uku,ranar suna zaune yan sanda suka shigo gida aka tattara su,aka tafi dasu,Ashe saurayin amirah tsohon barawo ne,anjima Ana Neman sa,shida abokan aikin sa,amirah tace batasan komai ba tace ita ai bata jima da zuwa garin ba,saurayin yace karya ne tare suke sata,suke komai itama tana cikin su,haka aka yanke masu shekara ashirin agidan yari,da hunkunci Mai wuya,kamar wasa amirah sunyi shekara uku a prison, ba abinda take tunawa sai mahaifiyar ta,wahala take sha sosai,saboda matan da suke cikin prison in,bawanda suke cin uba kamar amirah, koda ankawo sabon zuwa amirah ake sa tayi musu wanki,babu Mai tausayinta KO kadan,haka tayi tafama,dakanta tazo take addua Allah ya dauke ranta,wahala takai wahala kenan,amirah tacika shekara biyar da wata shida acikin prison,saurayinta ya aika sako akan amirah bata cikin su,asali ma batasan komai ba akan sana'ar dayakeyi,aka tambayeshi dalilin dayasa yamata haka,yace saboda bata tausayin mahaifiyar ta,yace duk iskanci sa ya rabu DA mahaifiyar sa lafiya,daga karshe aka sake amirah,aka sata cikin motor zuwa garin su,amirah ta dauki phone inta,tana kallon photo maman ta,sai kuka,har ta isa garin su.

  Amirah ta iso kofar gidan su,taga gidan kamar bana su ba,kofar gidan a rufe,wani Yaro Na zaune kofar gidan,tace Dan Allah matan gidan nan fa,yace shima bako ne,suna magana sai gawani yazo wucewa yace,wa nake gani kamar amirah tace eh,itace,yace ya kike Ina kika shiga shiru kin bata gaba ki daya,tace wallahi tafiya nayi,kana da labarin mama Na kuwa, naga kofar gidan a kulle,yace eh toh kije shagon Dan bala ki tambaye shi,Yakama hanya yatafi,amirah taje shagon Dan bala sukai magana,yace suje cikin gidan,ya bude gate in gidan,suka shiga,taga dakin maman ta ya kone da wuta,tace Ina mama na,Mai faru da ita,Dan bala ya nuna Mata kabari guda uku,yace wanchan Na mama,sauran Na kannen ki,gobara ce takama cikin dare,mun wayo gari muka samu gawa kawai,amirah tace yaushe haka ya faru?Dan bala yace yau shekara biyar kenan da wata shida, ranar da kika bar gari a Daren abin ya faru,haba amirah tasa kuka,wayyo mama Na,wallahi Na cuce kaina,ki gafarta mini,tayi ta ihu,wasu suka shigo cikin gidan saboda ihun amirah da suka ji,aka rarrashe ta,ahaka dai kullum amirah in tawaye gari, tafara kuka akan kabarin maman Nata,sai ta wuni tanayi,ba cin abinci,bayan wata uku,amirah tace Bari ta nema aikin yi,haka take bi gida gida tana karba wanki tana yi Ana biyan ta,wasu subata,wasu su hana ta, in tagama aikin,haka dai take fama,tazo tadaina wanki ta dawo sayar da abinci,shima mutane basa saya,wasu suci suki biyan kudi,haka fa take ta fama wulankanci iri-iri.
   Wata Rana ,amirah Na gida aka turo Yaro yayi sallama,Ana Neman ta a waje,tace kace Ina zuwa,bayan tafito taga wani mutun,baifi shekara talatin da biyar ba, a shekaru,suka gaisa,yace suna Na abdulhadi,nazo da niyar auren ki ne ni,so bawai Ina son wani bata lokaci bane,amirah tace aure?kasan KO ni wacece? Abdulhadi yayi dariya yace amirah ai inaga KO yaron da ba Haifa ba zai san da labarinki,bama niba,Dan haka kar kidamu duk wata shegan takanki nasani,kuma ahaka Zan aure ki,tace toh zanyi tunani,abdulhadi yayi dariya yace tunani kuma,toh shikenan kije kiyi tunani,anma ki tabbata kafin gobe kingama tunani,Dan ni taimaka miki zanyi,abin mamaki shine amirah bata bashi amsar dayace Mata taimaka Mata zaiyyi ba,kura tayi lafiya,washigari abulhadi yazo,amirah tace ta amince,acikin sati daya akayi komai,mutanen garin sai mamaki wai amirah tayi aure,abdulhadi yace zasu koma Kaduna da zama,hakan yasa amirah tasake bin mutane ta nema gafara su,tasame limamin unguwar su takara rokar sa gafara.
   
   Abdulhadi yana da mata biyu,yana son su sosai kuma,bayan amirah tayi wata biyu agidan,matan abdulhadi suka Fara galla Mata azaba,intakai Kara su,abdulhadi yace bata da hakuri,tacika mita,haka dai har tagaji dakai karar su,tayi shara,tayi wanke wanke,tayi abinci,ta wanke kayan yaran gidan,intayi abinci ace ba dadi,kamar wata Mai aiki,ranar dai tace tagaji abdulhadi ya sake ta,baza ta iya zama ba,abdulhadi yace ke har kina da bakin magana,ai haka zaki cigaba da hakuri,daga nan shima ya bude sabon page wulakanci,abinci ma Hana ta ci akeyi,so daya ake bata abinci,yanda kuka san baiwa,in dare yayi tayi ta famar kuka.
   
    Akwai wata tsohuwa da take yawan zuwa gidan su abdulhadi suna ce Mata kaka,akanyi abinci akai Mata,abdulhadi yana matukar son matan nan,yana kula da ita sosai,anma takan zo gidan duk ranar jumma'a ne,ranar kaka ta shigo gida,taga abdulhadi yana dukar amirah tace haba abdulhadi ba girman ka bane,tayi mishi fada sosai,ta kira matar gidan gaba ki daya,ta zaunar dasu tace maisa suke wulakanta amirah, sukace sun tsaneta ne haka kawai sukaji basa son ta,tayi musu fada,tace sudaina ba kyau,anan dai amirah tadan samu saukin wulakanci DA ake Mata,amirah takan je gidan kaka,suyi hira sosai,kaka tace amirah kibani labarin rayuwar ki,amirah ta kwashe labari ta bata,suna hira dare yayi,ruwan sama ya sauko,kaka tace amirah ta kwana agidan ta,zata fada wa abdulhadi,gashi sun kira wayar sa akashe,takira kishiyoyin ta suka ki daukawa,washigari da safe,amirah ta koma gida,tana shiga gida taga abdulhadi,yace dan ubanki Ina kika kwana,kinje yawon iskanci KO,nan ma karuwanci zakiyi,kafin tayi magana ya hau ta da duka,yace ya sake ta Saki uku,sauran matar sai murna,sai ga kaka ta shigo tace haba abdulhadi,Saki uku,toh agidana ta kwana,nace zanzo in maka bayani,ta kira wayar ka akshe,Ina sauran matan naka,takira su suka ki daukawa,kaka tayi musu kacha kacha ,ta zage su,ta nuna ranta ya baci,tace tunda ka saketa shikenan kaji dadi,amirah dauko kayanki mutafi,takama hannun amirah suka tafi.
   
   Bayan wata biyar,amirah tana jin dadin zama DA kaka,ta dauketa kamar mama,in tana zaune,ta tuna mahaifiyar ta,sai tasa kuka,kaka tace Dan Allah tadaina,ranar amirah tace tana son zuwa supermarket,takama hanya ta tafi,tadan gama zagawa,zata fita sai suka ci Karo da wani mutum,suka gaisa,toh shi wannan mutumin yana tare da mahaifiyar sa,alokacin tagansu suna magana da amirah, bayan yadawo maman shi tace wace wanchan yarinya,yace mama nima ban Santa ba yanzu muka hadu,tace kabita idan bata da aure Ina son ka aure ta,yace inshaa Allah mama,nan danan yabi amirah har ta tare keke-napep ya tsayar dasu,yace baiwar Allah inason magana dake,tace Ina saurare,Allah yasa ba laifi nayi ba,yace a'a,mahaifiyata tagan Mu tare tace lalle tana son in aure ki,dan haka Allah yasa baki da aure? Yace wallahi KO kina dashi sai ya sake ki,saboda ba abinda bazanyi ba in faranta wa mahaifiyata rai,wannan magana yasa amirah kuka,ta tuna mahaifiyar ta,irin rayuwar da sukayi tare,tace bani da aure,Kuma tunda mahaifiyar ka tabaka umarni,ni Kuma Na amince kodan ka faranta Mata rai,saboda idan baka faranta Mata rai ba watrana zaka so tana da rai,Dan kayi abinda take so anma bata a raye,hakan yasa suka karbe number juna,ta mishi kwatance gidan su,zai tafi tace ya sunan,yayi murmushi yace suna na alhaji ubale,tayi murmushi,suka rabu,yaje ya fada wa mahaifiyar sa yanda sukai da amirah,itama amirah tafada wa kaka komai,kaka tayi murna.
   
   Bayan an daura aure alhaji ubale da amirah,lokacin aure maman alhaji ubale tatafi Makkah,daga nan zata tafi hutu dubai,atakaice dai wata biyu tayi kafin ta dawo,kafin dawo ta,amirah taba mijin ta labarin rayuwar ta,ya tausaya Mata,yace tabbas ke abin tausayi ne,bayan mahaifiyar ubale ta dawo,dayake gefen ta daban ne ,tace bayanzu take son ganin amirah ba,sai ta huta,amirah hankalin ta yatashi,tace kotayi laifi ne,yace a'a haka mama take,ni kaina watrana cewa take bata son gani Na,kar kidamu,bayan sati biyu mama ta Kira su,suna zuwa gefen ta,amirah taga maman ta,ta goge idon ta,tasake budewa,tayi salati,tace mama,maman amirah tace amirah,haba sai kuka,amirah tace mama ki gafarta mini,mama Na tuba,mama ki yafe mini,dukkan su kuka,kannen amirah suka fito suka rungume amirah,alhaji ubale yayi murmushi,bayyi mamaki ba,saboda tunda amirah tabashi labari,yagane cewa itace amirah, yakuma gane dalilin dayasa maman amirah tace ya auro amirah,tace mama ance kin rasu,tace ban mutu ba,ai nasan kina Kaduna,Dan bala yakirani yafada min kin aure,amirah tace watau yasan kina raye?tace eh,amirah tace mama ya akai mijina ya zamo danki,maman amirah tace zanbaki labari anma bayanzu ba,labarin Nada tsayi,yanzu dai kibani labarin rayuwar ki,amirah tace mama ki gafarta min,tabbas naga masifa a rayuwa ta,nayi Dana sanin abubuwan Dana miki,maman amirah tace amirah Kullum addua nake miki,bantaba rike ki azuciya ba,Allah miki Albarka,yakuma albarkace auren Ku,tace kaikuma ubale ga amirah kanwar ka Kuma matar ka,a kula da ita,haka farin ciki ya dawo gidan,aka dauko kaka ,ta zauna agidan,amirah takai ziyara gidan tsohon mijin ta,suka ga yanda ta chanja,tayi kyau sosai,takai musu kyautar kayan abinci,amirah tadawo yarinya Mai kirki,tausayin mutane,bayan shekara biyu,Allah yayi Mata haihuwa,ta haife yan biyu,gida farin ciki.
Karshen labari Na kenan,nida Na rubuta Cmc,

ZAHRA'U

    Misalin karfe uku da rabi (3:30) na rana,Zahra'u Na shara,sai akace tabar sharan tazo ta sayo kayan miya a kasuwa,ta ajaye tsintsiyar, ta dauko hijabin ta har kasa takama hanya zata fita,sai Umar yace anty zarah Zan biki,tace bazaka Bini ba,sai Umar ya fashe da kuka,tace kaji yaron nan,zo Mu tafi,ta dauke shi a hannu suka fita,dayake kasuwan baida nisa sosai da gidan su zahra'u baifi tafiyar minti biyar,nan danan zahra'u ta isa kasuwa,ta saya abinda zata saya,ta kamo hanya zata fita daga kasuwa sai wani Mai wheelbarrow yazo ya ture ta,kayan hannun ta suka fadi duk suka zube,kafin tayi magana Mai wheelbarrow yayi salati ya jefar da barrow nashi gefe guda,yayi sauri ya kwashe tumatirin,albasa,da tattashe,groundnut oil kuwa ya zube bayanda zai kwashe wannan,ledar nama ta fashe,ya dauka aguje yaje ya wanke,ya nema wani Leda ya zuba Mata a ciki,zahra'u ta kasa ce komai,tana ta kallon mai wheelbarrow, abin mamaki shine yanda yake ta sauri gurin kwashe kaya,kuma taganshi a tsorace a frigice,sai ya kawo Mata ledar nama,yace hajiya, man gyadar(groundnut oil) ki kwalba nawa ne? Sai tayi murmushi tace Rabin kwalba ne,anan Mai barrow yasake dibawa aguje yaje ya sayo yakawo Mata,yace Dan Allah hajiya kiyi hakuri walahi bawai da gangan nayi miki haka ba,zahra'u tayi murmushi tace badamuwa tsautsayi ne,kuma yakan faru da kowa,Mai wheelbarrow yayi godiya,yace in bazaki damu ba in dauka miki kayan zuwa inda zakije,tace haba dan wannan ledar sai nasa a barrow ,nagode Allah saka da alkhairi,ta dauki Umar suka tafi gida.Zahra'u na isowa gida ta kwashe labari tafada wa kishiyan maman ta,suka ta dariya,Chan bayan wasu hour sai aga zahra'u ta fashe da dariya,in aka tambayeta sai tace ta tuna Mai wheelbarrow ne ,ranar dai gaba ki daya haka zahra'u ta kare tana dariya.
  
 Washigari da safe,bayan kowa yaci breakfast,mahaifin zahra'u zai fita aiki,kishiyar maman zahra'u bintu ,tace Mai gida,Ina son muyi magana yace toh! Anma sai ki hanzarta tunda kinga dai ni nake bude makaranta key suna hanu Na,(mahaifin zahra'u Mai gadi ne awani primary school),bintu tace maganar ma bazai dauki wani lokaci ba,suka ja gefe,tace mai gida jiya naga abin mamaki,yace Mai faru? Tace jiya Na aiki Zahra' u kasuwa,Mai gida, kasan abin mamakin? Yace sai kin fada,tace jiya dai zahra'u tayi dariya,mahaifinta yace Kai saboda Allah,bintu dagaske kike KO wasa,kinsan banason wasa da irin wannan magana,tace haba Mai gida in zanyi wasa ai bazanyi da irin wannan maganar ba,kasan yau shekara uku kenan da rasuwar mahaifiyar ta, yarinyar nan bata dariya,kuma maigida kasan Na dauke zahra'u kamar yar cikina,son danake Mata bana wa yarana Dana Haifa,Kai sheda ne maigida,yace eh wannan maganar naki gaskiya ne,kuma Allah zai saka miki da Alkhairi,shin kinsan Mai yasa ta dariya? Bintu ta kwashe labari tafada mishi,ya girgiza Kai,yace tabbas duk da bani da arziki,inshaa Allah zan nemo Mai barrow nan,in mishi kyauta Dan haka zandawo da wuri yau,yanzu ma dole ce tasa in fita in ba haka ba wallahi sai nashiga kasuwa Na nemo mai barrow nan tukun,yanzu Bari in samu inje kar in makara,bintu tace adawo lafiya maigida,yace Allah yasa,zaifita yaga zahra'u yace Mata zahra'u tace na'am baba,yace KO nima in Fara tura barrow ne ,haba kunya yakamata sai dariya,tagudu daki,hakan yasa shi murna yafita zuwa aiki.
  
       Bintu ta aiki zahra'u kasuwa,dalilin hakan kuwa shine Dan tana son taganta cikin farin ciki,sun matukar jin dadi ganin zahra'u na farin ciki,saboda tun rasuwar maman zahra'u aka kasa gane kanta,zahra'u najin za aiketa kasuwa, farin ciki Yakama ta, takama hanya zata fita,Umar yace anty Zan biki,tace zo mutafi kafin kasa min kuka,suka tafi kasuwa ,tana shiga kasuwa taga Mai wheelbarrow nan kuwa,shima ya ganeta,yazo ya gaisheta,in wuni hajiya tace suna na zahra'u ba hajiya ba,yace Allah sarki sunan kanwa ta,hakan yasa zahra'u murna,yace Mai zaki saya? ta fada mishi, haka suka zaga kasuwa,suna ta yawo,kunya ya hanata magana,shi kuma, ba mai son magana bane dama,taga wani abun hanu tace wannan abin hannun yamin kyau,yace dagaske tace eh,yace nima yamin kyau sosai,anma kinga irin Sana'a ta,banson kashe kudi akan abinda bai Kai ya kawo ba,tayi dariya tace kaidai mako yamaka yawa ,yayi dariya yace wallahi ba haka bane,sai tace wasa nake ma,bari in saya mana,yace a'a,Zan saya muna,haka suka ta jayayya dai akarshe yace ki saya min in saya miki,hakan akayi,kowa yabiya ma kowa,suna ta dariya,zata tafi tace zuwa anjima zakaji sako,yace sako! wani iri,tace hanzarin Mai kake,kajira mana,yace badamuwa Allah kaimu darai da lafiya,sai yace baki tambaye suna na ba,tace da kunya in tambaye sunan ka ai,sai yayi dariya yace suna na zahra'u ,tace Kai Na miji da sunan mace,yace eh,serious sunan na kenan,tace kodai zahradin kake nufi,yace a'a sunan shi zahra'u ,sai tawani kalle shi ,yayi dariya yace suna Na suleman,tace sunan kaka na ni kuma,sukai dariya,tace zahra'u suleman sai anjima,shi kuma yace suleman zahra'u sai anjima Ina kuma jirar sako,haka suka rabu kowa Na murmushi,abin Sha'awa in kagansu.
    
     Karfe hudu da Rabi,sai ga mahaifin zahra'u yadawo daga aiki,bintu ta kawo mishi abinci yana ci tana mishi hira,tace lalle magida yau ka dawo da wuri,yace bintu kema kinsan akan mai sunnan mama ba abinda bazan yiba,tace ni kuwa nasan da haka,tayi dariya,bayan yagama cin abinci,yace akira zahra'u,aka kirata,Baban yace ya sunan sirikin nawa,zahra'u tace siriki Kuma baba?yace eh mana KO bake son shine,zahra'u tayi murmushi,yace wasa nake miki mama Na,ya sunan shi? Tace suleman,yace daidai ina yake zama,ta mishi kwatance,yace yagane wurin,nan yasaka takalma,ya bude akukin kaza ya dauko zakara guda biyu,ya Kama hanya ya fita,zahra'u sai murna,bintu tace ohh!! Ni bintu ikon Allah zahra'u kindaina jin kunya Na,tace haba anty kinsan bazan daina jin kunyar kiba,bansan dalilin da Inajin magana akan Suleiman zanji Na rikice,yanzu kinga wanna abin hannun ban baki labari ba,shi yasaya min nima Na saya masa,bintu tace kice dai akwai sauran labari,hafsat,da Aisha suka shigo sukace umma keda zahra'u Suleiman ne,bintu tace zahra'u Suleiman kuma,sukace eh,bata baki labari ba,lalle anbarki a baya,bintu tace kuce ni Ina page one ,suka ta tsokalar zahra'u suna dariya,abin farin ciki ya samu,basu taba tsanmanni Zahra'u zata dawo cikin lafiyan ta sosai haka ba nan kusa.
   
Mahaifin Zahra'u ya iso kasuwa ya nemo seleiman, isowar Suleiman keda wuya yaga dattijo, abinda yazo azuciyar sa,sakon da zahra'u tace zai gani,anma Dan maisa zata aiko tsoho,shikadai dai yana magana a zuciyar sa,bayan ya iso,suka ka gaisa,mahaifin zahra'u yace suna na malam ubale,nine mahaifin zahra'u,sulieman najin haka ya sunkuya har kasa yace ina wuni baba,suka gaisa,yace batare da bata lokaci ba,Zan maka bayanin abin da yakawo ni,mahaifin zahra'u ya kwashe labari komai da rasuwar mahaifiyar zahra'u, halin da tashiga sannan dakuma haduwar su da Suleiman, bayan yagama mishi bayani,yace Dan haka ga wannan zakara guda biyu,kayi hakuri ni ba Mai arziki bane,Iya aBinda Zan Iya baka kenan,Suleiman yace haba baba,wallahi basai kabani komai ba,nagode wa Allah dayasa ni nayi sanadiyar sa wa yarku farin ciki,tunda nake a rayuwa ta,bantaba jin dadi irin wannan ba,Dan haka wallahi basai kabani komai ba,mahaifin zahra'u yace bakyau maida hannun kyauta baya,sannan akarshe inason kana Dan zuwa gida,burina Inga zahra'u cikin farin ciki,bance lalle kuyi soyayya ba,indai baka sonta,anma Dan Allah yanzu ne lokacin da muke bukatar ka,saboda rabon Mu da farin ciki agidan tun faruwar al'amarin Dana fada maka ,Suleiman yace inshaa Allah baba zan dinga zuwa,daga gobe inshaa Allah,haka suka rabu,Suleiman yayi hawaye,yace Allah nagode maka,sanadiya ta wata tasamu farin ciki.
    Mahaifin zahra'u yadawo gida,yafada wa bintu yanda sukai da sulieman,yakuma bashi izini yana zuwa gida hira,kuma Suleiman ya amince zaifara Zuwa gobe,hakan yasa aka fada wa zahra'u,jin dadin haka takasa bacci a daren saboda murna.
  Washigari,karfe biyar zahra'u taci kwalliya kamar sabuwar amarya,tajira Suleiman anma cikin ikon Allah baizo ba,har abinci ta mishi,taji haushi sosai,har su aisha suna Mata dariya suna tsokalar ta,sukace goben ma bazaizo ba,tace kut in baizo ba sai ta yanka su,bintu tace kar kidamu ba mamaki aiki ne ya Hana shi zuwa,Kuma kinsan irin aikin sa,zahra'u ta damu Anma aka rarrashe ta,washigari ma baizo ba,hafsat da Aisha sukace mun fada miki bazaizo ba,ranar kan bata musu dariya ba,ranta a bace,dasuka ga haka sai suka daina Mata wasar,suka dawo kwantar Mata da hankali,washigari ma haka,kwana hudu aka jera,Ana jiran Suleiman baizo ba,zahra'u tace zataje kasuwa ta duba shi,aka bata izini suka tafi tare da Aisha, banyan sun isa kasuwa suka nema shi,ba labarin sa,suka nema wuri suka zauna hour su uku suna zaune,aisha tace tagaji sutafi gida su dawo gobe tunda asabar ne,ba mamaki zaizo kasuwa,zahrau suka kama hanya bawai dan tana so ba,isowar su gida keda wuya zahrau tafashe da kuka,hankalin mutanen gida ya tashi,mahaifinta yace haba mama Na,kidaina kuka inshaa Allah da safe zanje Na dibo miki suleiman Kuma ni Zan kawo shi gida dakaina,da kyar aka rarrashe ta,gari Na wayewa karfe goma Baban zahra'u yatafi kasuwa har kusan azahar,tukun aka same wanda yasan Suleiman, aka tambaye shi Ina Suleiman yace ai yau kwana biyar kenan dayayi tafiya,yaje kauye,aka tambaye shi inane kauyen yace baisani ba,mutum daya ne yasan kauyen su Suleiman shi kuma yau da safe yatafi Lagos,abin haushin baida phone a hannun sa,mahaifin zahrau yayi salati,ya koma gida yayi wa bintu bayani haka aka ta rarrashin zahra'u .
   Bayan sati biyu,zahrau tafara rashin lafiya,ciwo kaman wasa ya kwantar da zahra'u, kafin dai ace wani Abu tayi wata biyu ba lafiya,Suleiman baizo ba kuma,tana fama da ciwo anma tana kirar sunan Suleiman, tana cewa baba Ina Suleiman, abin dai ba dadin fada,tazamo abin tausaya,tazo bata gane kowa,bata son magana ma,zafin ciwo yayi yawa,gidan ba walwala,Aisha tafashe da kuka,tace Dana Sani banyi Mata baki ba,Ina cewa Suleiman inta bazai zo ba,maman tace haba ai wasa kike Mata,haka dai akai wata hudu zahrau Na jinya,cikin ikon Allah sai tafara samun saukin jikin ta,Alhamdulilah,yanzu farin cikin gida yafara dawo wa,bayan sati uku,zahra'u takan Dan Iya fitowa ta zauna tsakar gida,ba magana dai sosai,har tafara kuma magana,tana Dan aikin gida,kaman wanke wanke,shara,aiki mara sa nauyi,ranar tace zataje kasuwa aka Hana ta zuwa,kusan kwana uku tayi tana tambaya,anma Ana Hana ta,shine dai tasake tambaya aka kyaleta,bayan ta tafi kasuwa ta dawo,tace tana jin jiri,akace ta kwanta tayi Bacci,Allah sarki zahra'u, kwanciyar da tayi ciwo ya dawo,lokacin da tashiga kasuwa tunanin Suleiman yadawo Mata,duk wanda tagani da barrow tace Mai Suleiman, hafsat ce take bada labarin saboda tare suka tafi,kuma a firgice zahra'u ta dawo gida,bintu tace shiyasa Na Hana ta Zuwa,malam kaikuma kace a barta,haka aka sake jinya Na wata hudu.
    Suleiman yana shigo gari sai gidan su zahra'u, yana isowa kofar gidan, yaga yara da goro a hannun su da sweet,yace bikin wa ake,Allah yasa ba zahra'u bace tayi aure,yana karaso kofar gidan,mahaifin zahra'u ya fito yaganshi,yace malam Suleiman Ina ka shiga,sulieman yace wallahi ranar da muka rabu dakai,aka kirani jikin mama Na ba lafiya,haka nakama hanya a lokacin,dare yamuna ahanya,barayi suka tare Mu,phone Ina da kudina duk aka kwace,Ina isa kuma DA kwana uku,rashin lafiya yakamani,haka Na shafe wata bakwai Ina jinya baba,sai da aka hada da maganin gargajiya,yanzu ma na Dan samu karfin jikina ne,nace dole inzo saboda bansan ya zahra'u take ba,ga wannan Dan uwa na sunan shi Ahmed mama tace dole muzo tare saboda yanayin jikin nawa kar yatashi bakowa kusa Dani,Baban zahra'u yace gaskiya ne,ai naje Na neman ka ba labarin ka,raina ya baci nace Dan baka son zahrau basai ka gudu ba Suleiman, anma Na fahimce ka yanzu,suna magana kenan,Suleiman yace baba Ina zahra'u, dafatan ba aure tayi ba,naga antaru,baba yace Suleiman kayi hakuri Allah yayi wa zahra'u rasuwa,sanadiyar rashin ka,tayi jinya wata takwas,baban ya fashe da kuka yace Allah sarki mama Na,kullum tace baba Ina Suleiman,nace zaizo,kullum haka muke fama da ita tace baba Suleiman,bamusan haka Zai faru ba,haka Allah tsara,Suleiman yayi salati,ya fadi ya suma,aka daga shi,aka watsa masa ruwa,bayan farfado, akai Mata sallah aka kaita,banyan anyi uku rasuwar zahra'u, yace zaitafi saboda jikin nashi,yaje yayi jinya agida,kafin yatafi,Baban ya dauko abin hannun zahra'u yace gashi inji zahra'u abaka wannan,ya karba yatafi yana kuka,ahmed yana bashi hakuri,Allah sarki zahra'u, yarinya Mai kunya,takamu da son Suleiman, lokacin da take tunanin farin cikinta ya samu ashe farin cikin Nata shine ajalin ta.
   Suleiman ya koma gida,baya Iya komai,yana zaune sunan Zahrau kawai yake Kira,sai yace suna Na zahra'u Suleiman,zahra'u sunan mace ne,Na miji da sunan mace,haka dai yake sanbatu abin tausayi,ahankali hankalin sa ya dishe.
Karshen labarin zahra'u Suleiman kenan,ni Wanda Na rubuta Cmc,nagode to everyone.